Ma Zhaoxu, ya bayyanawa taron kwamitin sulhun kan Jamhuriyar Afrika ta tsakiya cewa, yayin da yanayi a kasar ke gyaruwa, kasar Sin na goyon bayan kwamitin, ya duba yanayin da ake ciki da kuma buri da bukatun kasar, wajen daidaita wasu takunkumai.
Ya kara da cewa, manufar sanyawa kasar takunkumi ita ce, mayar da ita kan turbar zaman lafiya, da kiyaye doka da oda, yana mai cewa muhimmin abu a yanzu shi ne, taimaka mata wajen samun sulhu da zaman lafiya. (Fa'iza Mustapha)