in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU za ta bibiyi sahihancin zabukan Nijeriya da Senegal
2019-02-22 09:13:45 cri
Tarayyar Afrika AU, ta ce jami'anta masu sa ido kan zabuka, za su samar mata da sahihan rahotanni ba tare da bangaranci ba, game da ingancin zubukan Nijeriya na gobe 23 ga wata da na Senegal da za a yi ranar Lahadi 24 ga wata.

Wata sanarwa da AU ta fitar, ta ce yayin da kasashen biyu na yammacin Afrika ke daura damarar gudanar da sahihin zabe a karshen wannan makon, shugaban hukumar AU Moussa Faki Mahamat, ya bada umarnin tura jami'an sa ido kan harkokin zabe zuwa kasashen.

Nijeriya ta shirya gudanar da zaben shugaban kasa da na 'yan majalisun tarayya ne a gobe Asabar 23 ga wata, inda zaben Gwamnonin jihohi da na 'yan majalisun jihohi zai guda ranar 9 ga watan Maris.

Ita kuwa Senegal, za ta gudanar da zaben shugaban kasa ne a ranar Lahadi, 24 ga wata. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China