in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Trump ya ce babu gaggawa game da shirin kawar da makaman nukiliyar DPRK
2019-02-20 11:37:10 cri
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya fada a jiya Talata cewa, yana burin gani an samu cikakken shirin kawar da makaman nukilya daga zirin Koriya, inda ya bayyana cewa ba ya gaggawa wajen tsara wannan shiri.

Trump wanda ya bayyana hakan ga 'yan jaridu, inda ya ce yana duba yiwuwar ganawa da Kim Jong Un, shugaban kasar Koriya ta arewa (DPRK), a mako mai zuwa a birnin Hanoi na kasar Vietnam. "Ina tunanin abubuwa masu yawa za su biyo bayan taron," in ji shi.

Shugaban na Amurka ya ce, yana son a kai wani muhimmin mataki game da shirin kawar da makaman nukiliyar na DPRK, amma sai dai ya ce ba gaggawa yake ba, tun da har yanzu takunkuman dake kan Pyongyang suna nan daram har sai lokacin da kasar ta dakatar da dukkan shirinta na kerawa da gwajin makaman nukiliyar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China