in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bukaci a ingiza bangarorin kasar Yemen zuwa cimma tattaunawa mai ma'ana
2019-02-20 10:21:46 cri
Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya bukaci kasashen duniya su ingiza bangarorin kasar Yemen zuwa ga tattaunawa mai ma'ana.

Yayin taron kwamitin sulhu na MDD kan Yemen, Ma Zhaoxu ya ce ya kamata a ingiza bangarorin kasar zuwa ga cimma sulhu da yarjejeniyar siyasa mai dorewa, yana mai cewa ya kamata kuma su dage wajen ganin an bi ka'idojin MDD.

Wakilin na kasar Sin ya ce, suna fatan karkashin shugabancin kwamitin kula da tsagaita bude wuta a kasar, za a ga kyakkyawan kudurin shugabanci a aikace.

Ya ce suna fatan ganin an kaddamar da sabon zagayen tattaunawar zaman lafiya da wuri, bisa jagorancin manzon mussamam Martin Griffiths, ta yadda za a cimma sulhun da zai lura da bukatun dukkan bangarori tare da taimakawa wajen farfado da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Yemen. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China