in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta bukaci a takaita sanya takunkumi a daidaikun kasashe masu tasowa
2019-02-20 09:33:00 cri
A jiya Talata jakadan Najeriya a MDD ta bukaci a rage yawan takunkumai na wani bangare daya da ake azawa kan kasashe masu tasowa.

Sanya takunkumin na bangare guda ya sabawa 'yancin ikon kasa da dokokin kasa da kasa, kuma duk wani yunkuri na aza takunkumi kan wata kasa mai cin gashin kanta dole ne ya dace da dokokin yarjejeniyar MDD, inji Tijjani Muhammad-Bande, wakilin dindindin na Najeriya a MDD, wanda ya bayyana hakan a lokacin taron kwamitin musamman dake nazari kan yarjejeniyar dokokin MDD da kuma duba yadda za'a karfafa ayyukan hukumar.

Galibin takunkuman da aka sanyawa kasashe masu tasowa sun shafi kasashe mambobin kungiyar taryyar Afrika ne, da kungiyar kasashe 77 da kasar Sin, da kuma kungiyar kasashe 'yan ba uwanmu, in ji shi.

"Dole ne a rage karfin sanya takunkumin bangare daya, kuma a takaita wa'adin da ake dauka domin gujewa haifar da illa ga moriyar kasashen da abin ya shafa, da kuma al'ummomin kasashen," inji Bande.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China