Hukumar tsaro ta jamhuriyar Nijar ta sanar a jiya cewa, 'yan kungiyar Boko Haram sun kai harin kunar bakin wake a wani wurin karbar 'yan gudun hijira dake jihar Diffa ta kasar a ranar Lahadin da ta gabata, inda mata 2 suka ta da nakiyar dake jikunansu, tare da kashe kansu, gami da 'yan gudun hijira 3, da wani mazaunin wurin.
Kasancewar jihar Diffa dab da kan iyakar kasashen Nijar da Najeriya, ya sa ake ganin hare-hare masu yawa da 'yan ta'adda na kungiyar Boko Haram suke kai wa wurin, lamarin da ya haddasa asarar rayuka da yawa a shekarun nan.(Bello Wang)