in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Isra'ila ta tabbatar da soke taron kasashen gabashin Turai a birnin Kudus
2019-02-19 10:19:14 cri
Ma'aikatar harkokin wajen Isra'ila, ta tabbatar da soke taron kasashen gabashin Turai da aka shirya yi jiya Litinin a birnin Kudus, biyo bayan tsokacin da ministan ma'aikatar ya yi, game da alakanta al'ummar kasar Poland da 'yan Nazi.

A baya, an shirya cewa, taron zai gudana ne a jiya Litinin zuwa yau Talata, inda zai samu halartar kasashe mambobin kungiyar Visegrad da suka hada da Poland da Hungary da Jamhuriyar Czech da kuma Slovakia.

An fasa taron ne bayan sabon mukaddashin ministan harkokin wajen Isra'ila Yisrael Katz ya bayyana a ranar Lahadi cewa, jama'ar Poland sun hada hannu da 'yan Nazi yayin yakin duniya na II.

Da safiyar jiyan ne Jakadan Poland a Isra'ila Marek Morawiecki, ya bayyana tsokacin a matsayin abun kunya da kuma wariyar launin fata.

Daga baya kuma, Firaministan Poland din Mateusz Morawiecki ya soki tsokaci sannan ya sokewa ministan harkokin wajen kasarsa halartar taron.

Bayan Poland ta janye daga taron ne kuma Jamhuriyar Czech ta sanar da soke taron.

Tuni dai Firaministan Hungary Viktor Orban da na Slovakia Peter Pellegrini suka isa Isra'ila, inda kuma ake sa ran isar Firaministan kasar Czech Andrej Babis.

A cewar Ministan harkokin wajen Isra'ila, Firaministan kasar Benjamin Netanyahu, zai gana da shugabannin daya bayan daya, game da dangatakar dake tsakanin kasashensu. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China