A cewar gidauniyar Jack Ma, za a bada kyautar ne ga 'yan Afrika 10 masu sana'o'i, inda a kowacce shekara za a bada dala miliyan 1.
Za a bude shiga gasar cin kyautar ga dukkan 'yan Afrika ne a ranar 27 ga watan Maris, inda ake sa ran yin gasa ta karshe a nahiyar cikin watan Nuwamba.
Gidauniyar na da nufin karfafawa hazikan 'yan Afirka 100 masu sana'a gwiwa ya zuwa 2030, domin taimakawa nahiyar.
A watan Augustan bara ne Shugaban kamfanin na Alibaba, ya sanar da kafa wani asusu da zai karfafawa 'yan Afrika gwiwar cin gajiya daga tsarin tattalin arziki na zamani. (Fa'iza Mustapha)