in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran ta bukaci Turai su kara himma kan batun yarjejeniyar nukiliyar kasar yayin da Amurke ke neman janyewa
2019-02-18 12:46:17 cri
Ministan harkokin wajen Iran Mohammad Javad Zarif, ya bukaci manyan kasashen Turai da su kara kokari wajen ceto yarjejeniyar nukilyar Iran da aka cimma, kuma ya zargi Washington da yunkurin nuna karfin iko kan Iran.

Zarif ya bayyana hakan ne a lokacin taron kasa da kasa kan sha'anin tsaro na Munich, ya ce, ya kamata kasashen Turai su kara kaimi muddin suna son kiyaye dangantakar su da Iran, ya kuma kara da cewa akwai bukatar kasashen Turai su gabatar da tsarin tattaunawa na gamayyar hadin gwiwar kasa da kasa.

Kana Zarif ya ce, "Dole ne Turai su yi wani hobbasa muddin suna son kaucewa makircin Amurka na neman zaman zama saniyar ware," a cewarsa Iran a shirye take ta mutunta yarjejeniyar nukiliyar kasar ta shekarar 2015, wacce aka cimma da manyan kasashen duniya.

Jawabin da Zarif ya gabatar, yazo ne kwana guda bayan da mataimakin shugaban kasar Amurka Mike Pence ya bukaci kasashen Jamus, Faransa, da Birtaniya dasu goyi bayan Amurka wajen janyewa daga yarjejeniyar nukiliyar kana su daina neman kawo nakasu kan takunkuman da Amurkar da kakabawa Iran. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China