in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta bada umarnin sake bude kan iyakokinta bayan dage babban zaben kasar
2019-02-18 09:52:05 cri
A ranar Asabar gwamnatin Najeriya ta bada umarnin sake bude dukkan iyakokin kasar bayan dage zaben shugaban kasa da na majalisun dokokin kasar wanda hukumar zaben ta ayyana.

A ranar Alhamis ne Najeriya ta bada umarnin rufe dukkan iyakokinta domin samun nasarar gudanar da manyan zabukan kasar wanda a baya aka shirya gudanarwa ranar Asabar din da ta gabata.

A cikin wata gajeriyar sanarwa wanda babban kwantiloran hukumar shigi da fici na kasar, Muhammad Babandede, ya sanar, ya ce, an sake bude kan iyakokin kasar domin cigaba da zirga zirgar jama'a ta yau da kullum.

Babandede yace, jami'an hukumar shigi da ficin zasu cigaba da gudanar da ayyukansu na tsaron kan iyakokin kasar domin tabbatar da ganin dukkan wadanda ke shigi da fici ta hanyoyin kasa, sama, da ta ruwa suna da cikakku kuma ingantattun takardun da ake bukata.

Da sanyin safiyar ranar Asabar ne hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya ta sanar da dage manyan zabukan kasar inda ta kara mako guda, sakamakon wasu matsoli da suka sha kanta dake da alaka da kayan aiki. (Ahamd Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China