in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar harkokin wajen Sin: Sin na goyon-bayan kokarin da gwamnatin Venezuela ke yi na kare 'yancin kasar
2019-02-16 16:08:52 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Geng Shuang ya bayyana a jiya Jumma'a cewa, Sin ta dade tana goyon-bayan kokarin da gwamnatin kasar Venezuela ke yi na kare 'yancin mallaka gami da tabbatar da zaman karko a kasar.

Rahotannin da aka ruwaito sun ce, a kwanakin baya ne ministan harkokin wajen Venezuela ya ce, wasu kasashe ciki har da kasar Sin na yunkurin kafa wasu kungiyoyi don marawa gwamnatin Maduro baya, wadanda kuma nan bada dadewa ba za su dauki matakai don sanya kasashen duniya fahimtar irin hadarin da jama'ar kasar Venezuela suke fuskanta. Game da wannan batu ne, Geng Shuang ya bayyana cewa, kasarsa tana kira ga bangarori daban-daban da su goyi bayan dukkan jam'iyyun siyasar Venezuela, wajen lalubo bakin zaren daidaita rikicin kasar ta hanyar yin shawarwari cikin lumana. Kana kuma, Sin ta yi kira ga kasashen duniya da su mutunta ka'idoji gami da manufofin kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya, yana mai cewa bai kamata a rika tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasashen duniya ba. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China