in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta bukaci a sake zage damtse a kokarin kawo karshen bautar da yara a Afrika
2019-02-16 16:05:03 cri
Hukumar kula da ayyukan Tarayyar Afrika AU, ta bukaci kasashe mambobinta da abokan huldarta, da su hada hannu wajen kawar da matsalar bautar da yara a Afrika.

Hukumar ta ce duk da raguwar bautar da yara a duniya, abun takaici ne yadda har yanzu galibin kasashen da ake aiwatar da mummunar dabi'ar suka kasance a nahiyar Afrika.

Wata sanarwa da hukumar ta AU ta fitar a jiya, ta ce har kullum, nahiyar Afrika na cikin wadanda ke fama da matsaloli da rikice-rikice, wadanda ke kara hadarin bautar da yara.

A cewar wani rahoto na 2016, da ya yi kiyasin yaran da ake bautarwa a duniya, 1 bisa 5 na yaran nahiyar Afrika sun yi aikin bauta. Haka zalika, ya yi kiyasin yara miliyan 72.1 na cikin aikin bauta, kuma miliyan 31.5 na ayyuka masu hadari, wadanda suka fi yawa a bangaren aikin noma da hakar ma'adinai. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China