Hare-haren da aka kai wasu kauyukan Najeriya sun haddasa mutuwar mutane a kalla 66
An kai hare-hare kan wasu kauyuka 8 dake jihar Kadunan Najeriya a jiya Juma'a, inda 'yan sanda suka gano gawarwaki 66, ciki har da yara 22, yayin da aka garzaya da mutane 4 da suka ji raunuka zuwa asibiti. Rahotanni na cewa, zuwa yanzu, an riga an kama wasu da ake tuhuma da hannu cikin hare-haren, amma ba a sanar da sunaye da dalilinsu na kaddamar da hare-haren ba.
Da ma a yau Asabar aka shirya gudanar da babban zaben kasar, inda tun cikin watan Janairun bana, gwamnatin kasar ta gargadi tare da ambatar wasu wurare da rikici ka iya barkewa a lokacin zaben, ciki kuwa har da jihar Kaduna. (Bello Wang)