in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ba ta da niyyar yin takara da kasashen Latin Amurka
2019-02-14 20:26:57 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokion wajen kasar Sin Madam Hua Chunying ta bayyana a yau Alhamis cewa, kasarta ba ta da niyyar yin takara a yankin Latin Amurka ko ta halin kaka, kuma zargin da Amurka ta yi kan hadin-gwiwar Sin da kasashen Latin Amurka ba shi da tushe balle makama.

Rahotannin na cewa, a jiya Laraba, shugaban kasar El-Salvador Nayib Bukele ya zanta da mai taimakawa shugaban Amurka kan harkokin tsaro John Robert Bolton ta waya, inda ya ce El-Salvador babbar aminiyar Amurka ce. A nasa bangare Bolton ya ce, bangarorin biyu sun tattauna ne kan yadda za su karfafa zumuncin dake taakaninsu da yakar ayyukan kwace albarkatun da kasar Sin take yi a bangaren duniyarmu daga yamma.

Game da hakan, Madam Hua ta jaddada cewa, sam kasarta ba ta da niyyar yin takara a yankin Latin Amurka. Kuma hadin-gwiwar da kasar Sin take yi da kasashen Latin Amurka, ciki har da El-Salvador, hadin-gwiwa ce dake kawowa juna moriya, da nufin samun ci gaba kafada da kafada, al'amarin da ya kara inganta hadin-gwiwarsu.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China