in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Koriya ta kudu: Zagaye na biyu na tattaunawar DPRK da Amurka muhimmin mataki ne
2019-02-11 16:45:24 cri
Shugaban kasar Koriya ta kudu Moon Jae-in, ya fada a yau Litinin cewa zagaye na biyu na taron kolin tattaunawa tsakanin Koriya ta arewa (DPRK) da Amurka, zai kasance muhimmin mataki game da batun dakatar da shirin kera makaman nukiliya a zirin Koriya.

Shugaban na Koriya ta kudu ya ce, zagaye na biyu na tattaunawar DPRK da Amurka zai kara matsawa zuwa mataki na gaba inda ake sa ran daukar kwararan matakai game da kawar da makaman nukiliya daga zirin Koriya, da gyara alakar dake tsakanin Amurka da DPRK, da batun wanzar da zaman lafiya a zirin Koriya, wadanda dama su ne manyan batutuwan da aka amince da su tun a zagayen farko na tattaunawar tsakanin Washington da DPRK. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China