in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Koriya ta kudu zai tuntubi Trump kan batun zagaye na 2 na tattaunawar Amurka da Koriya ta arewa DPRK
2019-02-11 10:12:49 cri
Shugaban kasar Koriya ta kudu Moon Jae-in zai tuntubi shugaban kasar Amurka Donald Trump a wani lokaci a nan gaba game da batun shirya taron tattaunawa tsakanin shugaban kasar Koriya ta arewa (DPRK) da na Amurka Donal Trump, kakakin ofishin Blue House na Koriya ta kudu ne ya sanar da hakan.

Kim Eui-keum, kakakin fadar ta Blue House, ya shedawa 'yan jaridu cewa, shugabannin Koriya ta kudu da na Amurkar za su tattauna ne game da batun zagaye na biyu na taron tattaunawar DPRK da Amurka wanda ake sa ran shiryawa a nan gaba, yana mai cewa, har yanzu ba'a bayyana takamamman lokaci ba, amma a cewarsa nan ba da jimawa ba za'a kammala shirya taron ganawar.

Moon da Trump ana sa ran za su yi musayar kalaman ne ta wayar tarho a nan gaba kadan. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China