in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNECA ta bukaci a kara kokari yayin da nahiyar Afrika ke dauke da 'yan gudun hijira kusan miliyan 23
2019-02-09 16:14:34 cri
Shugabar hukumar MDD mai kula da tattalin arzikin Afrika UNECA, Vera Songwe, ta bukaci a kara kaimi wajen taimakawa 'yan gudun hijirar dake fadin Afrika.

Vera Songwe ta ce idan za a yi la'akari da adadin, 'yan ci rani miliyan 23 su rubanya adadin al'ummar kasar Tunisia, sannan sun kusa yawan al'ummar kasar Ivory Coast, wanda nauyi ne yanzu akan nahiyar.

Jami'ar ta bayyana haka ne yayin jawabinta a taron majalisar zartaswar AU dake gudana a hedkwatar kungiyar, wanda aka yi wa taken, 'yan gudun hijira da masu dawowa gida: lalubo mafita mai dorewa ga daidaitar al'umma a Afrika.

Shugabar ta bukaci shugabannin nahiyar su hada hannu wajen magance matsalolin dake haifar da rashin matsuguni ga matasa a nahiyar.

Ta ce tambaya a gare su wato shugabannin Afrika ita ce, yadda a matsayinsu na kungiya za su samar da nahiyar da suke muradi, idan za su rika barin matasa da 'yan mata suna kokawa a sansanoni, ba tare da sun jin kunyar hakan ba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China