in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 15 aka hallaka a yankin dake magana da yaren Turanci a Kamaru
2019-02-07 15:40:14 cri
Kimanin mutane 15 ne aka kashe yayin da wasu da dama aka jikkata su a jiya Laraba a yankin Bole-Bakundu, dake kudu maso yammacin yankuna biyu masu magana da yaren Turanci masu fama da tashe tashen hankula a jamhuriyar Kamaru.

"Ni da kaina na kirga gawarwakin mutane 15 maza da mata. Dukkansu an harbe su ne a kasuwa. Kuma ba masu dauke da makamai ba ne," wani mutum da ya ganewa idonsa faruwar lamarin shi ne ya bayyanawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua.

Akwai bayanai dake cin karo da juna dangane wadanda suka aikata kisan. Wasu mazauna yankin sun zargi dakarun gwamnati da laifin hallaka mutanen, amma a nata bangaren gwamnatin ta ce an kashe mutanen ne a sanadiyyar barkewar tashin hankali tsakanin dakarun sojojin gwanati da mayakan 'yan aware masu dauke da makamai. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China