in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamaru ta nemi afuwar Isra'ila bisa kalaman wani ministan ta na kyamar Yahudawa
2019-02-05 16:22:11 cri
Ministan watsa labarai, kuma kakakin gwamnatin kasar Kamaru Rene Sadi, ya ce kasarsa ta yi tir da kalaman wani ministan kasar masu kunshe da kyamar Yahudawa.

Cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Litinin Mr. Sadi ya nuna nadama ga kalaman da minista Jean de Dieu Momo ya yi ta kafar talabijin mallakar kasar.

Jami'in ya ce ministan harkokin hadin gwiwar kasar da kasashen waje, ya karbi bakuncin jakadan Isra'ila a kasar a ranar Litinin 4 ga watan nan na Fabarairu, inda ya bayyana masa takaicin gwamnatin kasar game da kamalan minista Momo, yana mai cewa ba da yawun gwamnati ya furta kalaman na batanci ba.

Rahotanni na cewa, minista Momo wanda ke aiki a ma'aikatar shari'ar kasar, ya kwatanta jami'iyyar adawar kasar ta CRM da Yahudawa, wadanda Hitler ya murkushe sakamakon dagawarsu. Mr. Momo ya yi wannan kalamai ne, yayin wata zantawa da wata kafar watsa labarai ta kasar. Jim kadan da hakan ne kuma, ofishin jakadancin Isra'ila dake kasar, ya bayyana matukar bacin ran sa da hakan, yana mai neman a baiwa Isra'ilan hakuri. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China