in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bangarorin dake rikici da juna a CAR sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya a Sudan
2019-02-03 15:40:11 cri
Bangarorin dake yaki da juna a jamhuriyar Afrika ta tsakiya (CAR), a jiya Asabar sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya a lokacin kammala wani taron tattaunawar zaman lafiya wanda ya gudana a Khartoum, babban birnin kasar Sudan, kamfanin dillancin labarai na SUNA shi ne ya ba da rahoton.

"Sassan da ba sa ga maciji da juna sun cimma matsaya kan wasu muhimman batutuwa dake suke takaddama kansu, kamar batun rarraba madafun iko, da kammala kafa gwamnati bisa adalci a cikin wa'adin da aka diba, wanda aka dade ana tattaunawa kansa," in ji Attal-Mannan Bakheet, shugaban masu shiga tsakani na bangaren Sudan, shi ne ya bayyana hakan.

"Daftarin farko na yarjejeniyar za'a sanya hannu kansa ne da yammacin yau Lahadi a gaban shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir da takwaransa na CAR," in ji jami'in.

Bakheet ya kara da cewa, za'a sanya hannu kan yarjejeniyar karshe kan daftarin ne a Bangui a babban birnin CAR a ranar Laraba mai zuwa, a gaban shugabannin kasashen dake makwabtaka da CAR.

Tun a ranar 24 ga watan Janairu, Khartoum take ci gaba da karbar bakuncin tattaunawar zaman lafiya tsakanin gwamnatin CAR da bangarori 14 da ba sa ga maciji da juna a kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China