Wata sanarwa da mai magana da yawunsa Laolu Akande ya fitar, ta ce jirkin helkwaftan mai cin mutane 6, na dauke da mataimakan shugaban kasar, da wasu masu tsaron lafiyarsa lokacin da hadarin ya auku, amma duk da cewa sassan jikin jirgin su kakkarye, babu wanda ya ji rauni sakamakon hadarin. Sanarwar ta kara da cewa, kwararru sun fara nazari domin zakulo musabbabin aukuwar lamarin.
Shi kansa mataimakin shugaban kasar ya bayyana ta shafinsa na twitter cewa, shi da dukkanin masu tallafa masa dake cikin jirgin sun kubuta lami lafiya, yana mai cewa masu tukin jirgin sun yi duk abun da ya dace domin kaucewa tasirin hadarin. (Saminu Hassan)