in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin harkokin wajen kasashen mambobin EU sun cimma ra'ayi daya kan raya huldar dake tsakanin kasashensu da Sin
2019-02-02 16:50:15 cri
Wakiliyar Tarayyar Turai EU, mai kula da manufofin diflomasiya da tsaro Federica Mogherini, ta bayyana a birnin Bucharest, fadar mulkin kasar Romania cewa, cikin kwarya-kwaryan taron ministocin harkokin wajen kasashe mambobin kungiyar EU na yini biyu, mahalarta taron sun cimma matsayi guda, kan yadda za su daidaita matsayarsu domin raya dangantaka da kuma karfafa mu'amalar dake tsakanin kasashensu da kasar Sin.

A yayin taron manema labaran da aka yi cikin hadin gwiwar Federica Mogherini da ministan harkokin wajen kasar Romania Teodor Melescanu bayan taron, Ms. Mogherini ta bayyana cewa, ministocin harkokin wajen mambobin kungiyar EU sun yi musayar ra'ayoyi kan yadda kungiyar EU za ta raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin. Ta ce, kasar Sin abokiyar kungiyar EU ce bisa manyan tsare-tsare, kuma muhimmiyar kasa ce cikin harkokin tattalin arziki da huldar ciniki da kuma batutuwan kasa da kasa da sauransu, lamarin da ya baiwa kunigyar EU damar raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin. Ta kara da cewa, EU tana son dukufa wajen habaka hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Sin.

Cikin shekarun baya bayan nan, kungiyar EU ta cimma nasarar karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Sin kan batutuwan da suka shafi fuskantar sauyin yanayi da kuma kiyaye yarjejeniyar nukiliyar kasar Iran da wasu harkokin kasa da kasa.

Shi ma a nasa bangaren, Teodor Melescanu ya nuna cewa, mahalarta taron sun bayyana fatansu na inganta hadin gwiwar dake tsakaninsu da kasar Sin a fannonin warware matsalolin kasa da kasa da fuskantar sauyin yanayi da sauran wasu batutuwa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China