Sin: A daidaita maganar Venezuela ta hanyar siyasa
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya furta a yau Jumma'a cewa, kasar Sin tana kira ga bangarori masu ruwa da tsaki da su yi shawarwari tsakaninsu, domin neman daidaita maganar Venezuela ta hanyar siyasa. Sa'an nan, a nata bangare, kasar Sin na son yin kokari tare da sauran bangarori daban daban domin daidaita lamarin. (Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku