in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: An cimma matsaya a taron kasashe 5 masu makaman nukiliya
2019-01-31 20:08:22 cri
Daga jiya Laraba zuwa yau, an yi taron kasashe 5 masu makaman nukiliya a birnin Beijing na kasar Sin. Don gane da batun, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Geng Shuang, ya furta a yau Alhamis cewa, a wajen taron kasashe 5 masu makaman nukiliya, wato Amurka, da Rasha, da Birtaniya, da Faransa, da Sin, an cimma matsaya ta fannoni 3:

Na farko, kasashen sun yi alkawarin daukar nauyin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya. Na biyu, sun sha alkawashin kiyaye tsarin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya. Na uku, sun ce za su ci gaba da musayar ra'ayoyi, musamman ma ta hanyar taron da za su rika shiryawa tsakaninsu.

A cewar Geng Shuang, wannan sakamako ne da aka samu, wanda zai karfafawa gamayyar kasa da kasa gwiwarsu kan yanayin tsaro a duniya. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China