in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe 5 sun sha alwashin kiyaye yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya
2019-01-31 10:42:35 cri

Kasashe 5 masu wakilcin din din din a kwamitin sulhun MDD, wato Sin, Faransa, Rasha, Birtaniya da Amurka, sun gudanar da wani taro a ranar Laraba a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin domin tattauna batutuwa dake shafar makaman nukiliya, inda suka sha alwashin yin hadin gwiwa da juna don kiyaye yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya.

Kasar Sin a shirye take a ko da yaushe wajen gina tsarin cimma daidaito da kawar da banbance banbance a tsakanin manyan kasashen biyar game da batun dabarun tsaro, da ba da gudunmowa wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankalin duniya, in ji Zhang Jun, shugaban tawagar wakilan kasar Sin, kuma mataimakin ministan harkokin wajen kasar, ya bayyana hakan a lokacin da yake tsokaci yayin kammala babban taron.

Kasashen biyar, wadanda ke amfani da makaman nukiliya bisa doka, sun fara shirya taro tun a shekarar 2009, da nufin ci gaba da tuntubar juna game da batutuwan da suka shafi kiyaye tsaron makaman nukiliya. Kasar Sin a halin yanzu ita ce mai sulhuntawa kan hadin gwiwar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China