in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: Bude taron kasashe masu makaman nukiliya wani sako ne mai kyau
2019-01-30 20:12:33 cri
A yau Laraba ne aka kaddamar da taron kasashe 5 masu makaman nukiliya a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, inda kasashen Amurka, Rasha, Birtaniya, Faransa da Sin, suka tura tawagogi domin halartar taron.

Dangane da hakan, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Sin Geng Shuang, ya furta a yau Laraba cewa, ta la'akari da yanayin da duniya ke ciki, yadda wadannan kasashe masu makaman nukiliya suka zauna tare, domin musayar ra'ayi kan al'amura masu alaka da tsaro, wani sako ne mai kyau ga daukacin al'ummomin duniya.

Babban jigon da ake tattaunawa a kai wajen taron shi ne " kara hadin kai don kiyaye tsarin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya a duniya". Sa'an nan kasashen 5, za su yi tattaunawa mai zurfi kan manufofi masu alaka da makaman nukiliya, da rage makaman, da hana yaduwarsu, gami da yin amfani da makamashin nukiliya ta hanyar lumana, da dai makamantansu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China