Wadanda suka ganewa idonsu faruwar lamarin sun bayyana cewa, fashewar bom din ta lalata gine-gine da dama dake dab da gidan man.
'Yan sanda sun bayyana cewa, kafin fashewar bom din, masu kiyaye tsaro sun shirya yin bincike kan motar dake tsaye a kofar shiga gidan man, jim kadan kuma bom din ya fashe a cikin wannan mota.
Har yanzu babu wata kungiya da ta dauki alhakin kai harin ba. (Zainab)