in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan karuwar cinikin da ake yi ta yanar gizo a karkarar Sin ya wuce na birane
2019-01-30 11:13:36 cri
Kamfanin ciniki ta yanar gizo na Alibaba na kasar Sin ya fitar da wani rahoto a jiya Talata, inda aka bayyana cewa, yawan karuwar cinikin da ake yi ta yanar gizo a yankunan karkarar kasar Sin ya zarce na wasu manyan birane da garuruwan kasar.

Kididdigar ta cewa, yawan karuwar cinikin da aka yi ta dandalin yanar gizo na kamfanin Alibaba a yankunan karkarar kasar Sin ya kai kashi 23.8 bisa dari a shekarar da ta shude, adadin da ya zarce na wasu manyan biranen kasar Sin da kashi 4.5 bisa dari, ciki har da Beijing da Shanghai da Guangzhou da kuma Shenzhen.

Rahoton ya bayyana cewa, adadin yawan bukatar da ake da ita a yankunan karkara zai kasance a matsayin wata muhimmiyar hanyar dake kara ci gaba sakamakon bunkasuwar hanyoyin ciniki na zamani, da karin damammakin amfani da shafukan Intanet da saurin samar da kayayyakin da ake bukata.

Har wa yau, yanar gizo za ta rage gibin dake kasancewa tsakanin yankuna masu ci gaban tattalin arziki dake gabashin kasar Sin da yankunan karkara marasa ci gaba na kasar.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China