in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin gwamnatin kasar Sudan za su tsagaita bude wuta a jihar South Kordofan, in ji shugaban kasar
2019-01-29 12:54:57 cri
Shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir ya sanar a ranar 28 ga wata cewa, sojojin gwamnatin kasar za su tsagaita bude wuta a jihar South Kordofan don sa kaimi ga kiyaye zaman lafiya da samun sulhu a tsakanin kabilun kasar. Kana ya kalubalanci dakaru masu adawa na SPLM da su shiga yunkurin shimfida zaman lafiya a kasar.

A wannan rana, shugaba al-Bashir ya sanar da tsagaita bude wuta a jihar South Kordofan yayin da yake halartar wani taron gangami da aka gudanar a birnin Kadoli, babban birnin jihar. Ya kuma jaddada cewa, gwamnatin kasar tana maida hankali tare da yin dukkan mai yiyuwa wajen tabbatar da zaman lafiya a dukkan fannoni a yankin.

Shugaba al-Bashir ya kalubalanci SPLM da ta shiga yunkurin shimfida zaman lafiya a kasar don kokarin samun ci gaba mai dorewa a yankin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China