in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar kasashen musulmi ta kira taron tattauna matakan tinkarar matsalar jin kai
2019-01-29 12:29:12 cri
Wasu hukumomin bada agaji na membobin kungiyar kasashen musulmi wato OIC a takaice, sun kira wani taro jiya Litinin a birnin Istambul na kasar Turkiyya, inda suka tattauna kan batun kulla wani sabon kawance mai suna OIC Red Network, don tinkarar matsalolin jin kai dake addabar kasashe membobin kungiyar.

Shugaban kungiyar bada agaji ta Red Crescent ta kasar Turkiyya Kerem Kinik ya bayyana cewa, a halin yanzu akwai mutane kimanin miliyan 135 wadanda ke bukatar taimakon jin kai a duk fadin duniya, ciki har da kashi 71 bisa dari wadanda ke zama a kasashe membobin kungiyar OIC. A waje guda kuma, daga cikin 'yan gudun hijirar da suka bar muhallansu sakamakon tashen-tashen hankali, akwai kashi 61 bisa dari wadanda ke zaune a yankunan kasashen kungiyar OIC.

A nasa bangaren, mataimakin shugaban kungiyar bada agaji ta duniya ta Red Cross Gilles Carbonnier ya bayyana cewa, kafa sabon kawancen zai taimaka ga tallafawa miliyoyin yara da tashe-tashen hankali da bala'u suka shafa a yankunan kasashen kungiyar OIC, tare kuma da inganta kwarewar kasashe membobin kungiyar ta fuskar samar da agajin jin kai.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China