in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai hari ga babban sansanin sojojin yaki da ta'addanci na kasar Burkina Faso
2019-01-29 11:07:59 cri
Hukumar kiyaye zaman lafiya ta kasar Burkina Faso ta sanar a ranar 28 ga wata cewa, an kai hari ga babban sansanin sojojin yaki da ta'addanci da sanyin safiyar wannan rana, wanda ya haddasa mutuwar sojoji a kalla 4.

Sanarwar ta bayyana cewa, da karfe 4 na sanyin safiyar wannan rana ne, dakarun suka kai hari kan babban sansanin dake arewacin kasar, lamarin da ya haddasa mutuwar sojoji a kalla 4 tare da raunatar mutane da dama. Kana dakarun sun kona wasu gine-ginen sansanin.

Ya zuwa yanzu, babu wata kungiya ko mutumin da ya sanar da daukar alhakin kai harin.

Tun daga shekarar 2015, aka kai hare-hare a kasar Burkina Faso, wadanda ke barazana ga halin tsaro a kasar. Ko a ranar 2 ga watan Maris na shekarar 2018, wasu dakaru sun kai hare-hare ga hedkwatar sojojin kasar dake birnin Ouagadougo da ofishin jakadancin kasar Faransa dake kasar, wadanda suka haddasa mutuwar sojoji 8. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China