in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta kafa sabuwar cibiyar kula da harkokin shige da fice
2019-01-25 09:29:26 cri
Hukumar kula da harkokin shige da fice ta kasar Sin (NIA) ta bayyana cewa, za ta kafa wata sabuwar cibiya a watanni shida na farkon wannan shekara, da nufin saukakawa baki 'yan kasashen wajen dake zuwa nan kasar Sin.

Cibiyar za ta samar da hidimar taimakon lauya, yare da al'adu ga bakin dake shigowa kasar ke bukata a lokacin da suke zaune da ma yin tafiye tafiye a cikin kasar ta Sin.

Bugu da kari, cibiyar gudanar da tsarin tattaunawa, da karbar rahotanni na korafe-korafe, da samar da taimakon gaggawa da kimanta da kuma wallafa muhimman bayanan gargadi a fannin tafiye-tafiye.

Hukumar NIA ta kuma bayyana cewa, nan ba da dadewa ba, za ta kaddamar da wani tsari ta yanar gizo da wata manhajar wayar salula, wadanda za su baiwa jama'a damar gabatar da bukatar neman takardun shiga ko fita daga kasar da biyan kudi da sanin abubuwan da ake bukata ta intanet da wayoyin salula na komai da ruwan ka.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China