in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Kamaru ta taimakawa sama da mutane 60,000 da suka rasa muhallansu a yankunan kasar da ake magana da Turancin Ingilishi
2019-01-23 11:18:27 cri
Ministan kula da harkokin yankuna na kasar Kamaru Paul Atanga Nji, ya bayyana cewa, gwamnati ta taimakawa sama da mutane 60,000 da suka gujewa matsugunansu a yankunan arewa maso yammaci da kudu maso yammacin kasar da ake magana da Turancin Ingilishi masu fama da tashin hankali.

Ministan ya bayyana hakan ne a birnin Yaounde, fadar mulkin kasar, yayin ganawa da wasu ministocin kasar guda 7 don tantance yanayin jin kai da ake ciki a yankunan biyu. Ya kuma shaidawa manema labarai cewa, baya ga wancan adadi, akwai kuma iyalai 1,200 da suka koma gidajensu.

Ya jaddada cewa, wajibi ne sauran kungiyoyin bayar da agaji dake da niyyar taimakawa mutanen da suka rasa muhallansu, su nemi izni daga gwamnati, don gudun taimakon nasu bai fada hannu 'yan ta'adda ba.

Jami'in ya ce, tuni aka kafa cibiyoyin tsugunar da 'yan tawayen da suka aje makamansu. ( Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China