in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IS ta kaddamar da sabon harin kunar bakin wake kan sojojin Amurka dake arewacin Syria
2019-01-22 10:13:13 cri
Kungiyar kare hakkin bil-Adama ta kasar Syria ta bayyana cewa, kungiyar IS ce ta kaddamar da harin kunar bakin wake da aka nufi kaiwa sojojin Amurka dake sintiri a lardin Hasakah dake yankin arewa maso gabashin kasar Syria da safiyar jiya Litinin.

Kungiyar ta ce, wannan shi ne harin kunar bakin wake na biyu da aka nufi kaiwa sojojin Amurkar cikin 'yan kwanaki a yankunan dake karkashin ikon Kurdawa dake arewaci da arewa maso gabashin Syria.

Rahotanni na cewa, harin ya jikkata sojojin Amurka biyu baya ga dakarun SDF dake karkashin ikon Kurdawa biyar da suka rasa rayukansu, lokacin da wani dan kunar bakin wake na IS ya tayar da wata nakiya da ya dana a cikin motarsa a wajen yankin kudancin Hasakah.

Ko da a ranar 16 ga watan Janairun wannan shekara ma, an ba da rahoton mutuwar sojojin Amurka 4, sakamakon wata nakiya da aka auna a kan jerin gwanon sojoji a birnin Manbij na arewacin Syria dake karkashin ikon Kurdawa. A lokacin, an dora alhakin fashewar kan kungiyar IS.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China