in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta samu karuwar samar da guraben ayyukan yi shekarar a 2018
2019-01-21 16:45:04 cri
Bisa ga alkaluman da hukumar kididdigar kasar Sin ta fitar a yau Litinin ya nuna cewa, karuwar samar da guraben ayyukan yi na kasar ta samu tagomashi a shekarar 2018.

Adadin sabbin guraben ayyukan yi da aka samar a yankunan biranen kasar ya kai miliyan 13.61 a shekarar 2018, inda ya karu da sama da gurabe 100,000 wanda ya dara na shekarun baya kana ya zarce hasashen da gwamnatin kasar ta yi tunda farko.

Adadin a shekarar 2018 ya karu sama da miliyan 13 a cikin shekaru 6 a jere.

Binciken ya nuna cewa adadin marasa ayyukan yi a yankunan biranen ya kai kashi 4.9 bisa 100 a watan Disamba, inda ya ragu da 0.1 bisa 100 idan an kwatanta da makamancin shekarar data gabata. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China