in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Isra'ila da Chadi sun dawo da hulda a tsakaninsu
2019-01-21 10:56:56 cri
A jiya ne firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu da shugaba Idriss Deby na kasar Chadi suka sanar da dawo da huldar diflomasiya a tsakanin kasashen biyu, kamar yadda ofishin firaministan Isra'ila ya sanar da hakan cikin wata sanarwa.

Sanarwar na zuwa ne bayan da Netanyahu ya isa kasar Chadi jiya da safe, ziyara ta farko da wani firaministan kasar Isra'ila ya taba kaiwa kasar dake da musulmi mafiya rinjaye.

Firaminista Netanyahu ya sanar cewa, baya ga dawo da huldar diflomasiya da kasar Chadi, Isra'ila za ta kulla hulda da wasu kasashen musulmi, amma kuma bai bayyana kasashen ba. Ya ce, wannan wani juyin-juya hali ne da suke gudanarwa a kasashen Larabawa da na musulmi.

Netanyahu ya yaba da kulla hulda da kasar Chadi, a matsayin misali na yadda Isra'ila za ta iya kulla hulda a nahiyar Afirka da gabas ta tsakiya, duk da tashin hankalin dake ci gaba da faruwa tsakaninsu da Falasdinawa.

Ziyarar da ya kai a kasar Chadi ta biyo bayan ziyarar aikin kwanaki biyu da Deby ya kai birnin Kudus ne a watan Nuwamban shekarar da ta gabata. A shekarar 1972 ne dai kasashen biyu suka katse hulda a tsakaninsu.

Galibin kasashen Larabawa da na musulmi dai ba su kulla alaka da kasar Isra'ila ba. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China