A cewar sanarwar, harin dai ya kasance martani ne da sojojin Amurkan suka mayar kan farmakin da dakarun al-Shabab din suka kai kan sojojin gwamnatin Somaliya a kwanakin baya, inda ba'a samu jikkatar fararen hula ba.
Rahotanni daga kamfanin dillancin labaran Somaliya sun ce, da safiyar jiya Asabar, wasu mayakan al-Shabab sun kai hari kan wani barikin soja a garin Kismayo dake kudancin Somaliya, inda sojojin gwamnatin kasar suka fatattaki mayakan, kafin daga bisani kuma suka dauki matakan sojan hadaka tare da sojojin Amurka dake Somaliya don kashe mayakan al-Shabab guda 73, tare da lalata wasu motocin kungiyar da dama.(Murtala Zhang)