in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Antonio Guterres: mun fi bukatar ra'ayin gamayyar bangarori da dama fiye da baya
2019-01-19 17:16:21 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya shirya taron manema labaru na farko na shekarar 2019 a jiya Juma'a, inda ya bayyana cewa, babu wata kasa dake iya gabatar da shirin warware matsalolin duniya ita kadai. "Yau mun fi bukatar ra'ayin gamayyar bangarori da dama fiye da kowane lokaci na baya."

Ban da wannan kuma, Guterres ya yi gargadin cewa, ya kamata kasashen duniya su tuna da tarihi, kada su manta da darussan da suka koya sakamakon yaduwar kalaman nuna kiyayya da suka dinga yaduwa a shekarun 1930. A cewarsa, "Kalaman nuna kiyayya barazana ce kai tsaye ga hakkin bil Adama da dauwamammen ci gaba da kuma zaman lafiya da tsaro."

Baya ga haka, Guterres ya waiwayi nasarar da MDD ta samu a bara a fannonin inganta tinkarar sauyin yanayi na duniya, da warware matsalolin 'yan gudun hijira da makaurata da dai sauransu. Game da kwaskwarimar da ake kokarin aiwatarwa ga tsarin MDD, ya ce, an riga an samu babban ci gaba a fannin, "duk abubuwan da muke yi a yanzu haka, abubuwa ne da muka taba yin alkawarin yin kwaskwarima a kansu." (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China