in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana fatan shirin ficewar Burtaniya daga EU zai gudana yadda ya kamata
2019-01-16 20:09:37 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta ce, kasarta na fatan shirin ficewar Burtaniya daga kungiyar Tarayyar Turai zai gudana yadda ya kamata.

Madam Hua ta bayyana hakan ne yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa kan tambayar da aka yi mata game da shirin Burtaniyar na ficewa daga EU.

A jiya ne 'yan majalisar dokokin kasar ta Burtaniya suka kada kuri'un kin amincewa da babban rinjaye kan yarjejeniyar ficewar kasar daga kungiyar ta EU. Mambobi 202 ne suka kada kuri'ar amince da yarjejeniyar yayin da 432 kuma suka kada kuri'ar kin amincewa da yarjejeniyar da gwamnatin Burtaniya da kungiyar ta EU suka amince.

Madam Hua ta ce, kasar Sin tana dora muhimmanci kan shirin ficewar Burtaniyar daga EU, tana kuma sane da wasu 'yan bambance-bambance a kasar da ma tsakanin Burtaniya da kungiyar EUn game da ficewar kasar daga kungiyar.

Ta ce, manufar kasar Sin game da bunkasa alaka tsakanin Sin da Burtaniya da kuma Sin da EU ba za ta canja ba. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China