in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Oxford Economics: Kasar Sin ita ce kawar sauran kasashen dake yankin Asiya da tekun Pasific a fannin ciniki
2019-01-16 13:57:07 cri
Oxford Economics, wata cibiyar nazarin harkokin tattalin arziki ta kasar Birtaniya, ta fitar da wani rahoton bincike a jiya Talata, inda ta ce kasar Sin za ta ci gaba da kasancewa abokiyar hadin kai mafi muhimmanci a fannin ciniki ta sauran kasashen dake yankin Asiya da tekun Pasific, kuma wannan yanayi ba zai canza ba cikin shekaru masu zuwa.

Rahoton ya nuna cewa, tun da kasar Sin ta zama mambar kungiyar ciniki ta duniya WTO a shekarar 2001, tattalin arzikin ta, da na sauran kasashen dake yankin Asiya da tekun Pasific ke kara hadewa waje guda, kana kowanensu na dogaro kan cinikayyar da ake yi tsakaninsu matuka.

Yanzu haka da yawa daga cikin kasashen dake yankin Asiya da tekun Pasific suna fitar da mafi yawan kayayyakinsu zuwa kasar Sin, kana sun fi shigo da kayayyaki daga kasar Sin, idan an kwatanta da na sauran kasashe.

An ce, ko da yake saurin karuwar tattalin arzikin kasar Sin ya dan ragu, amma ana ci gaba da hasashen ganin kasar ta kasance wuri mafi muhimmanci da sauran kasashen dake yankin Asiya da tekun Pasific suke fitar da kayayyakinsu. Saboda yadda ake kokarin shiga tsarin samar da kayayyaki na yankin Asiya, da neman tura kaya zuwa kasuwannin kasar Sin, ita ce manufa mai muhimmanci ga yawancin kasashen dake yankin Asiya da tekun Pasific, a kokarinsu na raya masana'antu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China