in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin tsaron MDD ya bukaci warware rikicin zaben jamhuriyar dimokaradiyyar Congo cikin lumana
2019-01-16 11:16:41 cri
Mambobin kwamitin tsaron MDD, sun bukaci sassa masu ruwa da tsaki, da su tabbatar da warware sabanin da ya biyo bayan zaben shugabancin jamhuriyar dimokaradiyyar Congo, bisa tanajin dokokin kasar.

Cikin wata sanarwa, mambobin kwamitin sun ce tuni aka riga aka gabatar da korafe-korafe, gaban kotun tsarin mulkin kasar, suna kuma karfafa gwiwar daukacin masu ruwa da tsaki, da su kare yanayin zaman lafiya da aka samu yayin babban zaben da ya gabata, su kuma bi hanyoyin warware sabani da kundin tsarin mulkin kasar, da ma tanaje-tanajen dokokin zaben kasar suka shimfida.

Kwamitin ya ce, yana fatan dukkanin sassan kasar za su kauracewa ta da hankali, su martaba zaman lafiya da lumana da aka samu yayin babban zaben, da ma sakamakon da aka cimma. Kaza lika su mutunta dimokaradiyya, tare da zaman lafiya da lumanar kasar.

Har ila yau, mambobin kwamitin sun yi kira da a tabbatar da hadin kan kasa, da ginin ta bisa tsarin zaman lafiya, da tattaunawar siyasa tsakanin dukkanin masu ruwa da tsaki. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China