in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ali Bongo ya jagoranci bikin rantsuwar kama aiki na gwamnatin Gabon
2019-01-16 10:42:19 cri
Shugaban kasar Gabon, Ali Bongo Ondimba, ya jagoranci bikin rantsuwar kama aiki ta sabuwar gwamnatin kasar a jiya Talata. Wannan shi ne karon farko da ya halarci wani biki a Gabon, tun bayan da ya tafi ketare don jinya a watan Oktoban bara.

An gudanar da bikin ne a fadar shugabancin kasar, inda mambobin gwamnatin 38 suka yi rantsuwar kama aiki. Bayan haka, sabon firaministan kasar Julien Bekale, ya bayyana wa kafofin watsa labaru cewa, yadda shugaba Bongo ya halarta, da kuma jigorantar bikin, ya karyata jita-jitar da aka yada, cewa lafiyar jikinsa ta tabarbare.

An ce shugaban ya koma gida a daren ranar 14 ga wata, sai dai ba a bayyana ko zai sake komawa jinya a kasashen waje ba.

Ali Bongo ya dade yana samun jinya a ketare, tun daga watan Oktoban bara. Kana an ga fuskarsa a baya bayan nan ne a jawabin sa na taya muryar sabuwar shekara da ya gabatar wa jama'ar kasarsa, ta wani bidiyon da aka dauka.

A ranar 7 ga watan nan, an yi yunkurin wani juyin mulki a Libreville, fadar mulkin kasar, wanda bai samu nasara ba, inda sojoji masu ta da kayar baya suka ce Ali Bango, ba zai iya ci gaba da mulki ba sakamakon tabarbarewar lafiyar jikinsa. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China