Rahotanni sun ce maharan sun farwa kauyen Rann mai nisan sama da kilomita 170 daga birnin Maiduguri da yammacin Litinin. Kaza lika wasu mayakan kungiyar sun farwa kauyen Damasak.
A kuyen Rann, mayakan kungiyar sun kone asibiti, da makaranta, da sauran gine-ginen gwamnati. Sun kuma yi yunkurin karbe sansanin sojojin gwamnati dake wurin. An ce an yi dauki ba dadi tsakaninsu da sojojin, kafin daga karshe sojojin su fatattake su
Rundunar sojojin kasar dai ba ta fitar da sanarwa a hukumance game da harin ba tukuna. (Saminu Hassan)