in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabar babban taron MDD ta yaba da gudummawar kasar Sin
2019-01-15 19:32:58 cri
Shugabar babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 73, Madam María Fernanda Espinosa ta zanta da 'yan jaridun kasar Sin a kwanan baya, inda ta ce, Sin muhimmiyar abokiyar hadin-gwiwa ce ta MDD, wadda ta yi alkawarin goyon-bayan ra'ayin kasancewar bangarori daban-daban a harkokin duniya.

Madam Espinosa ta kuma yaba da gudummawar da kasar Sin ta bayar ta fannin tinkarar matsalar sauyin yanayi, inda ta ce, Sin ta yi matukar kokari wajen magance matsalar sauyin yanayi, kana ta cika alkawarinta a wannan fanni.

Har wa yau, yadda kasar Sin ta yi nasara tsame mutane sama miliyan 700 daga kangin talauci ya baiwa madam Espinosa kwarin-gwiwa sosai. Ta ce, hakika wannan gagarumar nasara ce, kuma Sin babbar kasa ce dake taimakawa ga cimma muradun MDD na samun dauwamammen ci gaba nan da shekara ta 2030.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China