in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutanen Kamaru na damuwar yawaitar garkuwa da mutane a yankin Adamawa
2019-01-14 11:18:22 cri
'Yan siyasa, jami'ai da masana harkokin shari'a suna ci gaba da nuna damuwarsu dangane da yawaitar matsalolin yin garkuwa da mutane a yankin Adamawa mai yawan tsaunuka.

"Adamawa na fuskantar hali mafi muni a tarihi. Mun damu matuka. Yin garkuwa da neman kudin fansa ya zama ruwan dare a wannan yankin. Kauyuka sun koma kufai kuma tattalin arziki ya sukurkuce," Theophile Baoro, wani wakilin al'ummar yankin Adamawa, shi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a yayin da matsalar ke cigaba da ta'azzara.

An samu rahotannin yin garkuwa da mutane a yankin sama da guda 150 a cikin shekarar da ta gabata, kamar yadda mahukunta yankin suka bayyana. An kiyasta hasarar kudin kasar CFA miliyan 500, kwatankwacin dala dubu 900 wadanda aka biya a matsayin kudin fansa. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China