Bayan aukuwar hadarin, gwamnatin birnin Shenmu ta fara daukar matakan daukin gaggawa, inda aka tura ma'aikatan ceto wurin don gudanar da aikin ceto da tallafawa mutanen da abun ya shafa.
A waje guda kuma, ma'aikatar kai daukin gaggawa ta kasar Sin ta tura wata tawaga zuwa wurin, don bayar da jagoranci ga ayyukan ceto da gudanar da bincike kan aukuwar hadarin. A halin yanzu ana nuna himma da kwazo wajen gudanar da ayyukan ba da tallafi da ceto da binciken musabbabin aukuwar hadarin.(Murtala Zhang)