in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yang Jiechi ya gana da ministan harkokin wajen Saliyo
2019-01-12 16:19:30 cri
Jiya Jumma'a, mamban hukumar siyasa na kwamitin tsakiyar jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kana shugaban ofishin kwamitin kula da harkokin waje na kwamitin tsakiyar kasar Sin Yang Jiechi, ya gana da ministan harkokin wajen kasar Saliyo Alie Kabba a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

A yayin ganawar tasu, Yang Jiechi ya bayyana cewa, a shekarar 2018 da ta wuce, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban kasar Saliyo Madda Bio, a yayin taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka wanda aka yi a birnin Beijing, inda shugabannin biyu suka cimma matsaya kan wasu manyan batutuwa. Kasar Sin tana son zurfafa zumuncin gargajiya dake tsakaninta da kasar Saliyo, karfafa fahimtar juna dake tsakaninsu a fannin siyasa, habaka hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu bisa dukkan fannoni, karfafa mu'amalar dake tsakanin kasashen biyu kan harkokin kasa da kasa da na shiyya-shiyya, domin kiyaye moriyar kasashen biyu, har ma da dukkanin kasashe masu tasowa.

A nasa bangare kuma, Mr. Kabba ya ce, shugaban kasarsa Madda Bio, ya cimma nasarar ziyarar aiki a kasar Sin a shekarar 2018. Kasar Sin ita ce aminiyar kasar Saliyo, shi ya sa, kasar Saliyo tana fatan yin hadin gwiwa da kasar Sin domin ci gaba da inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China