in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya bukaci aiwatar da matakan cimma muhimman kudurori a tsarin gudanar da gwamnati
2019-01-11 19:58:34 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bukaci aiwatar da matakan cimma muhimman kudurori a tsarin gudanar da gwamnati. Shugaban wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin koli na JKS, ya bayyana hakan ne a Juma'ar nan, yayin cikakken zama na uku na hukumar sa ido da ladaftarwar JKS karo na 19.

Shugaban ya ce akwai bukatar fadada kwazo, wajen inganta ayyukan jam'iyya, da kuma tabbatar da cimma manyan kudurori, da gudanar da ayyukan gwamnati bisa doka.

Xi, wanda kuma shi ne shugaban hukumar zartaswa ta rundunar sojojin kasar Sin, ya ja hankalin masu ruwa da tsaki, wajen ci gaba da aikin tabbatar da wanzuwar nasarorin da aka riga aka samu a fannin yaki da cin hanci. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China