in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Sin ya gana da ministan wajen kasar Saliyo
2019-01-11 19:14:31 cri
Wang Qishan, mataimakin shugaban kasar Sin, ya gana da minista mai kula da hakokin waje da hadin kai da kasashen ketare na kasar Saliyo, Alie Kabba, a yau Jumma'a, a birnin Beijing dake kasar ta Sin.

Yayin ganawar, babban jami'in kasar Sin ya ce, ya kamata kasashen 2 su yi kokarin yaukaka dankon zumuncin dake tsakaninsu, da kara musayar ra'ayoyinsu game da harkokin da suka shafi kasashen 2, da sauran sassan duniya baki daya. Za a kuma kara kokarin aiwatar da manufofin da aka gabatar wajen taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana bara.

A nashi bangaren, ministan wajen kasar Saliyo, ya ce kasarsa na son koyon dabarun raya kasa na kasar Sin, da zurfafa hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen 2, da kara kyautata huldar dake tsakaninsu.

A nasa bangare, mamban majalisar gudanarwa kuma ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, shi ma ya gana da mista Alie Kabba.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China