in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan hare-hare na barazana ga cigaban yammacin Afrika da yankin Sahel: in ji wakilin MDD
2019-01-11 11:04:53 cri
A sakamakon karuwar hare haren kungiyoyi masu tsattsauran ra'ayin addini, wadanda suke yin amfani da karin dabaru irin na zamani, suna haifar da koma baya ga cigaban kasashen yammacin Afrika da yankin Sahel, wakilin MDD mai kula da shiyyar ne ya bayyana hakan ga kwamitin sulhun MDD a ranar Talata.

"Daukar matakan soji, duk da cewa sun zama tilas, amma hakan ba zai wadatar ba" inji Mohamed Ibn Chambas, wakilin musamman na babban sakataren MDD a yammacin Afrika da yankin Sahel, ya jaddada bukatar daukar matakan da suka dace.

A yankin tafkin Chadi, akwai karuwar hare haren mayakan Boko Haram a watannin baya bayan nan, mayakan na kokarin yaki da dakarun sojojin da aka girke a yankunan, in ji shi, ya kara da cewa, ana cigaba da samun rikicin manoma da makiyaya, amma ya ragu.

A Nijer, duk da tura dakarun tsaro da na wanzar da zaman lafiya, har yanzu, suna cigaba da fuskantar kalubaloli a yankunan yamma da kudancin kasar," in ji wakilin MDD.

Duk da karuwar matsalar kalubalolin tsaro, Chambas ya yaba da yadda aka gudanar da zaben shugaban kasa a Mali a bara, da zabukan wakilan shiyyoyi a kasar Mauritania, da kuma zabuka a kasashen Togo da Cote d'Ivoire, ya kara da cewa, duk da irin cigaban da aka samu wajen tabbatar da tsarin demokaradiyya a shiyyar, akwai bukatar cigaba da kokari wajen shawo kan kalubalolin da suka shafi harkokin zabuka a shiyyoyin."

Wakilin MDDr yace, akwai bukatar daukar matakan da suka dace, kasancewar a cikin watanni 6 masu zuwa shiyyar zata tunkari manyan zabuka masu yawa da suka da kasashen Najeriya, Senegal, Mauritania da jamhuriyar Benin.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China